22 Afirilu 2019 - 17:55
Ghana: Ana Zargin Wasu ‘Yan Najeriya Da Sace Jakadan Estonia

Jami’an tsaron kasar Ghana sun sanar da cewa, wasu mutane sun sace jakadan kasar Estonia da ke birnin Accra, amma an samu nasarar kwato daga hannun wadanda suka yi garkuwa das hi.

A cikin bayanin da rundunar ‘yan sandan kasar ta Ghana ta fitar, ta tabbatar da cewa an sace jakadan na Estonia a kasar Ghana Nabil Makram Basbous ne a cikin unguwar da yake zaune a lokacin da yake motsa jiki, kuma ana zatin cewa wasu ‘yan Najeriya ne su uku suka sace shi a safiyar Alhamis da ta gabata.

Sai dai rundunar ‘yan sadan ta kasar Ghana ba ta bayyana sunayen mutanen ba, amma ta ce tana da bayani a kansu, kuma tana ci gaba da bin diggin lamarinsu domin cafke su.

Wannan dai shi ne karon farko da aka sace jakadan wata kasa a kasar Ghana, wanda hukumomin kasar kuma suka zargi ‘yan Najeriya da aikatawa, duk kuwa da cewa mahukuntan Najeriya ba su ce uffan a kan batun ba.